Sheikh Dr Ahmad Abubakar Gumi ya bayyana cewa yin azumin sittu Shawwal ba shi da asali, hasali ma yinsa bidi’a ce bisa wani babi da ya karanto daga cikin Muwadda Maliku.
Sheikh Gumi ya yi karatun ne a 20 ga watan Oktobar 2018, sai dai ya wallafa karatun dai dai lokacin da al’ummar musulmi ke daukar niyyar fara azumtar kwanaki 6 na watan Shawwal kamar yadda DaboFM ta tabbatar.
Daga cikin littafin Muwadda wanda Sheikh Gumi ya karanta ya ce; “Yin azumi 6 bayan an bude baki, na Ramadan. Ban taba gani daga magabata ba. Bai zo min cewa wai yana azumin bayan Ramadan ba, kuma suna tsoron ma zai iya zama Bidi’a.”
Binciken DaboFM ya gano inda Shiekh Gumi yake cewa hadisan da malamai ke kafa hujja da su akan azumin Shawwal ba inganta bane.
Wannan Hadisin da ake rawaito wa “Wanda ya raka azumin Ramadan da azumtar kwanaki 6 na Shawwal…’ Bidi’a ne.”
Sai dai malamin irinsu Sheikh Muhammadu Bn Uthman Kano, sun soki fatawar malamin har ya fitawar da Jahilci, – Jahilci ne baƙiƙƙirin wani jahili yace azumin ‘Sittu Shawwal’ ba Sunnah bane – Bn Uthman Kano
