Wata gidauniyar jinkai mai sunan, Hadeeyatul Khair Foundation, da wasu matasan mata a jihar Kano ke jagoranta, sun shirya baiwa makarantar Firamaren dukkanin abinda take bukata.
Hakan na zuwa ne bayan wani rahoto da DABO FM tafitar a ranar 5 ga watan Disamba, wanda ya nuna irin halin ko in kula da makarantar take ciki na rashin dukkanin wasu muhimman kayayyakin karatu.
A wata sanarwa da kungiyar ta fitar ta hannun shugabarta, Mufida Fari, ta bayyana shirinsu na ziyartar makarantar domin kai taimako.
“Suna bukatar kusan dukkanin kayyakin karatu da suka hada da ginin ajujuwa, kujeru, tebura, litattafai da kayyakin rubutu.”
Shugabar ta bayyana zasu fara kaiwa makarantar Litattafai da kayayyakin rubutu a ranar Lahadi, 22 ga watan Disamba, sa’an ta shiga shirin tattaro kudade don gyaran makarantar baki daya.
“A wannan makon, 22/12/19, zamu fara kai ziyarar makarantar domin rarraba musu litattafai da kayayyakin rubutu.”
Shugbar ta kara shaida bin wasu daga cikin Gidauniyar jinkan al’umma domin samu isassun kudaden aiwatar da ayyukan da makarantar take bukata.
