Home LabaraiGwamnan jihar Borno bai iske Likita ko 1 ba a ziyarar bazata da ya kai asibitin Gwamnati

Gwamnan jihar Borno bai iske Likita ko 1 ba a ziyarar bazata da ya kai asibitin Gwamnati

by Dabo Online
0 comments

Gwamnan jihar Borno, Babagana Zulum, ya kai ziyarar bazata zuwa asibiti a garin Maiduguri da sauran ma’aikatun gwamnati.

Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa Gwamnan Babagana bai iske ko da likita kwara daya ba a ziyarar bazatar da yayi zuwa asibitin Umaru Shehu da karfe 1 na dare.

Jaridar tace babu Likita ko daya daga cikin likitoci 19 da suke aiki a asibitin.

Sai dai ya iske Ungozomomi 10 daga cikin 135 wadanda zasuyi aiki a ranar.

Rahotan yace gwamnan ya kira Likitocin a waya domin jin bahasin dalilin rashin zuwan nasu, amma 10 daga cikinsu basu amsa wayar ba.

Haka zalika, rahotan yace gwamnan ya iske ‘yan tsirarun Likitoci a ziyarar da yakai asibitin asibitin kwararru na jihar da misalin karfe 2 na dare.

GWamnan ya bayyana rashin jin dadinshi bisa yacce ake karbar marasa lafiya a Asibitocin.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00