Gwamnatin ta bayyana haka ne ta hannun Kwamishinan kananan hukumomi na jihar, Alhaji Bello Dankande, a wani taro da yayi da Sarakunan gargajiyar jihar.
“Kowacce masarauta zata samu mutum 100 hadi da 500 da muka dauka daga farko. Zamu girke wasu a gidajen mai domin hana ‘yan bindigar samun mai.
Yace Gwamnatin bazata lamunci a cigaba da tashin hankali a fadin jihar ba.
“Abin ya isa haka, bazamu bari a cigaba da wannan kisan kiyashi da akeyi a jihar mu ba.”
“Gwamnatin tarayya data jiha nayin iyakacin kokarinta na yaki da ‘yan ta’addar.