0
Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta lallasa takwararta ta jihar jihar Jigawa wato Jigawa Golden Stars da ci 2 babu ko daya a cigaba da bugun wasanni ajin Firimiya.
Wasan da kungiyar ta Kano Pillars ta buga a yau Lahadi, 15 ga watan Maris na 2020 a filin wasa na Sani Abacha dake jihar Kano ya kasance wasa na 24 da kungiyar ta buga a kakar bana.
Dan wasan kungiyar, Auwalu Ali Mallam ne ya jefa dukkanin kwallaye guda biyun inda ya fara jefa ta farko a bugun daga kai sai mai tsaron gida a minti na 29 kafin daga bisani ya jefa ta biyu a minti na 62.
Pillars tana mataki na 4 da maki 34 yayin da Jigawa Golden Stars dake kan mataki na 19 da maki 26.
