Mata ta rikito da mijinta daga kan kafar bene, bayan da tace ya cije ta a unguwar Dorayi dake birnin Kano.
Matar mai suna Rashida Sa’idu Muhammad, tace wata ‘yar hatsaniya ce ta hadosu da mijinta, wacce ta samo asali bayan ta kamashi yasa handsfree a lo yana waya da wata budurwa a cikin gida.
Rahila, tace tayi kokari kwace wayar daga hannun mai gidan nata, lamarin daya janyo suka fara kokawar da har takai da mijin ya gantsara mata cizo a hannu.