Ko kasan Victor Odungide, Wanda yayi iƙirarin kashe shugaba Buhari idan har ya zarce?

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

A kwanakin bayan gaf da gudanar da zaben shugaban kasar Najeriya, wani matashi mai suna Victor Odungide yayi furucin da yayi nuni da son ya kashe shugaba Muhammadu Buhari.

CC4E1A52 4EDD 42CB 9CAB 997EAE8349EC - Dabo FM

Victor yayi wannan furuci ne daidai lokacin da  shugaba Buhari ya wallafa wani sako a shafinshi na Twitter, inda yake bayyanawa al’ummar Najeriya cewa bazai raba kudi daga asusun kasar ba domin yakin neman zabe.

87EDE87E 8061 4FE7 9904 AA3570A461F9 - Dabo FM

Tin a lokacin da Victor yayi wannan furuci, kamfanin na Twitter suka dakatar dashi domin ya saba ka’idar ta kamfanin ya gindaya nayi barazanar rai ga wani mai amfani da manhajin.

Bayan bincike da wakilanmu suka gudanar, mun gano cewa Victor ya bude sabon account na twitter da suna mai suna @Victor_odungide, wanda har mukayi kokarin jin matsayarshi akan batun kisa shugaba Muhammadu Buhari.

Sai dai har lokacin da muka hada wannan rahotan, kimanin awanni biyar bai bamu amsa ba.

4226D4E0 942C 4BDD B352 0F3D63D9870C - Dabo FM

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00