0
Shugaban Rundunar ‘yan sandan Najeriya IG Muhammad Adamu yayi wa kwamashinonin ‘Yan Sanda 13 karin matsayin zuwa mataimaka na II a matakin kasa.
Bayan Karin wannan matsayi shugaban Rundunar ya tura kowanne su zuwa bakin aiki daban-daban; yasu sun tsinci kan su a yankunan rundunar wasu kuma cikin makarantu Hukumar ‘Yan Sanda.
Wannan Karin matsayi da kuma kama aiki, ya fara nan take ne in ji shugaban.
Shugaban ya hore su da su kasance masu mai da hankali yayin aiki, su kuma saka ido sosai don tabbatar da zaman lafiyar al’umma.
Wadanda wannan Karin matsayi ya shafa dai sun hadar da:
- AIG Dan Bature,fdc – AIG DFA FHQ
- AIG Hyelasinda Kimo Musa – AIG PMF
- AIG Yunana Y. Babas, mni– AIG Zone 8 Lokoja
- AIG Dan Mallam Mohammed,fdc – AIG SPU
- AIG Mua’zu Zubairu Halilu – AIG CTU
- AIG Rabiu Yusuf – AIG ICT
- AIG Ahmed Iliyasu – AIG Zone 2, Lagos
- AIG Mohammed Uba Kura – AIG Maritime
- AIG Zaki M. Ahmed – AIG Zone 6, Calabar
- AIG Zama Bala Senchi – AIG Community Policing
- AIG Bello A. Sadiq – AIG Zone 1, Kano
- AIG Austin Agbonlahor Iwero,fdc – AIG DOPS FHQ
- AIG Lawal Ado – AIG Works
Kowanne su ya fara aiki nan take.
