Home LabaraiMakarantu a garin Garo dake jihar Kano na cikin halin ko-in-kula

Makarantu a garin Garo dake jihar Kano na cikin halin ko-in-kula

by Muhammad Isma’il Makama
0 comments

Garo dai itace mahaifar kwamishin kananan hukumomi Alhaji Murtala Sule Garo, da kuma wasu manya da suka rike madafun iko a Najeriya.

Ƙauyen Alkalawa da ke mazaɓar Garo a cikin ƙaramar hukumar Kabo a jihar Kano, na fama da matsalar rashin ajujuwan makaranta a ƙauyen na su.

Sai dai kuma bayan ‘yar kwarya-kwaryar bincike da Dabo FM tayi, mun gano makarantun wannan gari na cikin halin ko in kula ta ganin yadda dalibai ke daukar darasi a mazaɓar Garo da ke jihar Kano.

Ilimin Furamare na ƙara samun koma baya a wasu daga ƙananan hukumomin jihar Kano duk da kuɗaɗen da gwamnatoci ke warewa fannin na ilimi.

Ƙarancin kujerun zama da kayan aiki na koyo da koyarwa na ci gaba da kassara karatun ‘ya’yan talakawa a waɗannan ƙananan hukumomi.

Matsalar rashin ajujuwan ta sanya al’ummar wannan ƙauye yin amfani da karan Masara da na Gero wajen yin rumfar da ƴaƴansu za su dauki darasi a ciki.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00