Home Kiwon LafiyaRashin motsa jiki yana kisa irin na masu shan ‘Tabar Tabako’ da masu Kansa

Rashin motsa jiki yana kisa irin na masu shan ‘Tabar Tabako’ da masu Kansa

by Dabo Online
0 comments

A yanzu, rashin motsa jiki yana kawo asarar rayuka matuka kamar yacce masu shan taba suke mutuwa a fadin duniya.

DABO FM ta binciko wani bincike da masana kiwon lafiya a fannin cutar daji dake kasar Birtaniya suka gudanar akan tasirin da rashin motsin jiki yake wajen haifar da cutar daji musamman ta Mama dake damun mata yanzu.

A yayin binciken bayan kwarya-kwaryar binciken, sun gano cewa yakan haddasa cututtuka irinsu ciwon sigar, ciwon zuciya da kansar dake kama babban hanji.

Binciken da aka wallafa a mujallar Lancet, ya tabbatar da cewa kashi kaso 3 bisa 4 na mutanen da shekarunsu ya wuce 18 basa motsa jiki wanda bisa dalilin haka ake samu mutane miliyan 5.3 a kowacce shekara.

DABO FM ta tattaro cewa; a mutuwa 10 wacce cutar ciwon zuciya, ciwon siga da kansar hanji suka zama sanadi, guda 10 ciwon ya kamasu saboda rashin motsa jikinsu.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00