Home LabaraiShugaba Buhari ya sanya hannu a kasafin kudin shekarar 2020

Shugaba Buhari ya sanya hannu a kasafin kudin shekarar 2020

by Dabo Online
0 comments
Buhari Signs

Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaba hannu kan kasafin kudin shekarar 2020 a yau Talata, 17 ga watan Disambar 2019.

A yau ne dai shugaban yake cika shekaru 77 a duniya, wacce tazo dai dai da ranar da shugaba ya sanya hannu a kasafin kudin Najeriya.

Naira tiriliyan 10.59 ne kudin da shugaban ya sanya wa hannu.

DABO FM ta tattaro cewa taron ya samu halarci mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, shugaban Majalissar Dattijai, Sanata Ahmad Lawan, shugaban Majalissar wakilai, Femi Gbajabiamila da sauran manyan mukarraban gwamnatin Najeriya.

Shugaban ya bayyana cewa; “Yau rana ce mai dadi, na sanya hannu a kasafin kudi a ranar da nake cika shekara 77 a duniya.”

“Nayi murnar yacce Majalissar Tarayya tayi hubbasa wajen aminta da wannan kasafin cikin tsari. Yanzu tsarin kasafin kudin ya dawo Kasafin da akeyi a watan Disamba zuwa Janairu.”

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00