Home LabaraiShugaban gudanarwa a ma’aikatar kashe gobara ta jihar Kano, ya rasu

Shugaban gudanarwa a ma’aikatar kashe gobara ta jihar Kano, ya rasu

by Dabo Online
0 comments

Babban shugaban gudanarwar hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Sagir Madaki, ya rasu yau Talata a jihar Kano.

Kakakin hukumar, Sa’idu Muhammad Ibrahim ne ya shaidawa Jaridar Kano Focus.

Ya bayyana cewa mamacin ya mutu ne a Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano da misalin karfe 4:45pm.

Zuwa yanzu an kammala jana’izar mamacin kamar yacce addinin Musulunci ya tanada a masallacin unguwar Yola ta jihar Kano, kamar yacce KANO FOCUS ta rawaito.

Marigayi Sagir Madaki, ya rasu yana da shekara 7, bar mata 1 da ‘ya’ya 7.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00