Home Labarai‘Yan Shi’a sun kashe DCP Umar Usman tare da cinnawa motocin ‘NEMA’ wuta

‘Yan Shi’a sun kashe DCP Umar Usman tare da cinnawa motocin ‘NEMA’ wuta

by Dabo Online
0 comments

An bayyana Kungiyar ‘yan uwa musulmi ta IMN da alhakin kisan DCP Umar Usman, mataimakin yan sanda a birnin tarayyar Abuja.

DABO FM ta binciko cewa; duk dai a yayin gudanar da zanga-zangar, yan Shi’a sun kone motocin hukumar bada agajin gaggawa ta NEMA kamar yacce duk Jaridun suka tabbatar.

Daga cikin motocin da ‘Yan kungiyar suka kone.

A cikin makon da muke ciki dai shugaban ‘yan sandan Najeriya, ya haramta dukkanin wata zanga-zanga a wasu titunan birnin tarayyar Abuja.

Sai dai DABO FM ta tabbatar da bijirewa umarnin rundunar yan sandan da kungiyar ta Shi’a tayi bisa hujjarsu ta cewa “Su ba zanga-zanga sukeyi ba.”

A ranar Litinin dai kungiyar ta cigaba da gudanar da zanga-zangarta domin neman saki shugabanta dake tsare a hannun gwamnati bisa umarnin Kotu.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00