1
Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar Covid-19 guda 11 a daren Talata.
Kamar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 373.
“A yau da misalin karfe 11:00 na dare an sake samun masu dauke da cutar ‘Corona Virus’ guda 11. An samu guda 11 a Lagos.”
