‘Yar Najeriya mai shekaru 21 tayi fice bayan kammala karatun kiwon lafiya a kasar Turkiyya

by Dabo Online
0 comments

Yar Najeriya mai shekaru 21 da ta kammala karatun digirinta a fannin “Nursing” ungozoma tayi fice a cikin daliban kasashen waje da suka kammala karatun tare.

Maryam Ahmad Abdulhamid, yar asalin jihar Jigawa ta kammala karatun nata ne a jami’ar Near East University dake Nicosia, babban birnin kasar Cyprus wacce take makokantaka da kasar Turkiyya a tarayyar Turai.

Maryam mai shekara 21 ta kammala karatu da sakamakon kusan mafi kyawu a cikin kafatanin daliban makarantar inda tayi zarra a cikin daliban da suka kammala karatun ungozomanci.

BD249FDE DC2D 4095 9E65 EB1B377B7326 - Dabo FM

Wakilinmu ya rawaito Maryam ta shafe shekaru 4 tana karatun inda a kowacce shekara ta kan samu sakamako mafi kyawu daga sauran dalibai abokan karatunta.

An dai haifi Maryam a shekarar 1998 a garin Malam Madori dake jihar Jigawa, jihar dake arewa maso yammacin Najeriya.

C4AC0D86 FCF0 4520 9C93 0E46B9252D79 - Dabo FM

913255D6 CA6C 402B 9462 1A6C78391060 - Dabo FM

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00