0
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi umurnin cewa kada kowani minista da ya tafi kasar waje sama da sau biyu a kwatan zango.
Ministoci za su iya fita wajen kasar ne sau takwas kacal a shekara, ministan labarai, al’adu da yawon bude ido, Lai Mohammed ya bayyana. Kamar jaridar Legit ta ruwaito.
Bayan nan, kada kowani minista dake ziyarar aiki a kasar waje ya tafi da hadimai wadanda ke da muhimmanci a tafiyar sama da guda hudu.
Daga yanzu jami’an gwamnatin tarayya da ke kasa da mukamin ministoci za su kasance da hadimai kadan. Sannan daga yanzu ba za a dunga lissafin kudin tafiya a kan kowani sa’a ba.
