Home LabaraiSojoji sun fatattaki Boko Haram a yunkuri harin Damaturu

Sojoji sun fatattaki Boko Haram a yunkuri harin Damaturu

by Dabo Online
0 comments

Rundunar Sojin Najeriya tace ta samu nasarar dakatar da wani hari da kungiyar Boko Haram tayi yunkurin kai wa a garin Damaturu na jihar Yobe.

Tin da yammacin Lahadi, wasu mazauna yankin suka shaidawa DABO FM jin karar harbe-harbe wanda ta kai ga wasu sun kauracewa yankin.

Kakkakin sashen ‘Operation Lafiya Dole’, Laftanar Chinonso Oteh ne ya tabbatar da fatattakin da jami’an suka yi wa Boko Haram a harin da sukayi yunkurin kaiwa zuwa garin.

Tini dai aka cigaba da gudanar da rayuwa a garin dake kusa da babban titin Gashua a garin Damaturu.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00