0
Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar COvid 19 guda 4 a safiyar yau Lahadi.
KAmar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 25.
Da wayewar safiyar yau da misalin karfe 8:05, hukumar tace ta samu karin cutar guda 4, tace guda 3 a jihar Legas, 1 a jihar Oyo.
Jerin jihohin da aka tabbatar;
Lagos- 19
Abuja- 3
Ogun- 2
Ekiti- 1
Oyo- 1
Jimilla: 26
