Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar Covid-19 guda 10 a daren Alhamis.
Kamar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 184.
“A yau da misalin karfe 08:00 na dare an sake samun masu dauke da cutar ‘Corona Virus’ guda 10. An samu guda 7 a Lagos, 3 a Abuja.”
Ga jerin adadin da aka tabbatar a kowacce jiha;
Lagos – 98
Abuja – 38
Ogun – 4
Inugu – 2
Ekiti – 2
Oyo – 8
Edo – 4
Bauchi – 3
Osun – 14
Rivers – 1
Binuwai – 1
Kaduna – 4
Ten new cases of #COVID19 have been reported in Nigeria; 7 in Lagos and 3 in the FCT.
As at 08:00 pm 2nd April there are 184 confirmed cases of #COVID19 reported in Nigeria. Twenty have been discharged with two deaths pic.twitter.com/XWSSLVi7Zq