Home LabaraiBabban LabariCoronavirus: Kasar Saudiya ta dakatar da zuwa aikin Umrah

Coronavirus: Kasar Saudiya ta dakatar da zuwa aikin Umrah

by Rilwanu A. Shehu
0 comments

Labarin da ke shigo mana Yanzu, yayi nuni da cewa kasar Saudiya ta dakatar da al’ummar Musulmi zuwa aikin Umrah. A jiya ne dai Gwamnatin kasar ta fidda wannan sanarwa.

Dakatarwar ta biyo bayan gujewa kamuwa da cutar Zazzabin Mashako (Coronovirus) da kasar tayi.

A cewar hukumomin kasar, Yanzu haka sun girgiza saboda kamuwa da cutar da makwantanta sukai, don haka wannan shi ne matakin da ya kamata kasar ta dauka don kare kanta.

Yanzu haka dai, an dakatar da duk kan kasashen duniya zuwa aikin Ibadar na Umrah.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00