Gidauniyar wasu ‘yan mata a Kano ta kai tallafin kayan abinci da tufafi zuwa gidan marayu da gidan yari

by Dabo Online
0 comments

Gidauniyar Hadeeyatul Khair da wasu mata a jihar Kano suka kafa ta kai tallafin kayan abinci da tufafi zuwa gidan marayu da gidan yari a jihar Kano.

A ranar 7 ga watan Julin 2019 ne dai gidauniyar ta kai ziyararta ta farko zuwa gidan Marayu dake Nassarawa a jihar Kano, inda suka rarraba kayan abinci, kayan sakawa dama daffafen abinci domin ciyar da mazauna gidan.

Kayayyakin sun hadar da Sabulan wanki, Sabulan wanka, Madara, Biskit, Chizi, Lemuka da Gurasa.

E73629BE 4E5C 4387 9F17 62F0C4D45F40 - Dabo FM
Wasu daga cikin kayyakin da Gidauniyar ta rarraba.

Duk dai a ranar 7 ga watan Juli, Gidauniyar Hadeeyatul Khair ta kai ziyarar tallafin zuwa gidan yari dake Goron Dutse ta jihar Kano.

3ABFB231 1FAC 4066 871E FD24A9EA87CF - Dabo FM
Yayin Ziyarar Gidauniyar zuwa gidan yari na Goron Dutse, Kano

Shugabar hulda da jama’a ta gidauniyar, Pharm Rukayya Kabir Abbas ta bayyanawa DABO FM cewa sun kafa gidauniyar ne domin bada tasu gudunmawar ga tallafawa marasa karfi da niyar rage musu radadin da zafin rayuwa.

D72D73ED 873D 4BDF 8B84 D8E16FE598E8 - Dabo FM
Yayin ziyarar Gidauniyar zuwa gidan Marayu dake Nassarawa, Kano

70DA6DE2 1784 49E1 9B7C 716D633BC568 - Dabo FM

90787B20 BE99 42EC B87E FBB5C938DA46 - Dabo FM

Karin Labarai

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00