Home LabaraiNan gaba duk dan takarar shugaban kasar da yazo yana muku kuka to kuyi ta kanku -Shehu Sani

Nan gaba duk dan takarar shugaban kasar da yazo yana muku kuka to kuyi ta kanku -Shehu Sani

by Muhammad Isma’il Makama
0 comments

Tsohon sanatan Kaduna, Kwamared Shehu Sani ya bayyana talakawa kada su kara yarda da duk wani dan takarar da zai zo yana wa talakawa yan koke-koke domin yaudare ce zallar ta.

Majiyar DABO FM ta bayyana Sanatan yayi wannan furici ne a fejikan sa na sada zumanta a yammacin ranar Juma’a.

Shehu Sani yace “Daga yanzu duk dan takarar shugaban kasar da ya sake zuwa muku dauke da farin hankici yana koke-koke to kuyi ta kanku [domin zallar yaudara ce.”

Wannan yana zuwa ne bayan mawuyacin halin da yan kasar suka fada daga karbar mulkin shugaba Buhari, wanda a wannan takin shugaban kasa Buhari ke shan zazzafar adawa.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00