Home LabaraiRikicin Kano zai iya shafar Masarautun Arewa – Attahir Bafarawa

Rikicin Kano zai iya shafar Masarautun Arewa – Attahir Bafarawa

by Dabo Online
0 comments
Attahir Bafarawa

Tsohon gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Attahir Bafarawa ya ja hankalin cewar rikicin kirkirar sabbin masarautu a jihar Kano ka iya shafar shafar sauran masarautun jihohin arewacin Najeriya.

A yayin wata hira da tsohon gwamnan yayi da sashin Hausa na Muryar Amurka, DABO FM ta tattaro tsohon gwamnan yana bayyana cewa lallai sarauta zata lalace idan ana yi wasu masarautun.

Yace; “Maganar ayi masarautu a Kano ba ta ko taso ba, in dai ana haka, sarauta za ta lalace a Arewa.”

Ya bayyana cewa shugaba Muhammadu Buhari ne kadai zai iya shawo kan lamarin a matsayinshi na shugaban kasa kuma dan Arewa.

Shima a nashi bangaren yace baya goyon bayan rarraba masarautun kuma bai kamata a siyasantar da sarauta ba musamman irin ta jihar Kano.

Yace; “Bai kamata azo ana wasa ana sa siyasa a masarauta irin ta Kano ba.”

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00