Home Kiwon LafiyaYanzu yanzu: An samu karin mutum 20 masu dauke da Coronavirus, jumilla 131 a Najeriya

Yanzu yanzu: An samu karin mutum 20 masu dauke da Coronavirus, jumilla 131 a Najeriya

by Dabo Online
0 comments

Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar Covid-19 guda 20 da daren yau Litinin.

Kamar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 131.

“A daren yau da misalin karfe 9:00 an sake samun masu dauke da cutar ‘Corona Virus’ guda 20.”

“An samu guda 13 a Legas, 4 a Abuja, 2 a Kaduna da guda 1 a jihar Oyo.”

Ga jerin adadin da aka tabbatar a kowacce jiha;

  • Lagos – 81
  • Abuja – 25
  • Ogun – 3
  • Inugu – 2
  • Ekiti – 1
  • Oyo – 8
  • Edo – 2
  • Bauchi – 2
  • Osun – 2
  • Rivers – 1
  • Binuwai – 1
  • Kaduna – 3

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00