Home Kiwon LafiyaYanzu yanzu: An samu karin mutum 23 masu dauke da Coronavirus, jumilla 174 a Najeriya

Yanzu yanzu: An samu karin mutum 23 masu dauke da Coronavirus, jumilla 174 a Najeriya

by Dabo Online
0 comments

Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar Covid-19 guda 23 a daren Laraba.

Kamar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 174.

“A yau da misalin karfe 08:00 na dare an sake samun masu dauke da cutar ‘Corona Virus’ guda 23. An samu guda 9 a Lagos, 7 a Abuja, 5 a Akwa Ibom 1 a Bauchi da Kaduna.”

Ga jerin adadin da aka tabbatar a kowacce jiha;

  • Lagos – 91
  • Abuja – 35
  • Ogun – 4
  • Inugu – 2
  • Ekiti – 2
  • Oyo – 8
  • Edo – 4
  • Bauchi – 3
  • Osun – 14
  • Rivers – 1
  • Binuwai – 1
  • Kaduna – 4

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00