Home Kiwon LafiyaYanzu yanzu: Wadanda Coronavirus ta kama a Najeriya sun zama 111

Yanzu yanzu: Wadanda Coronavirus ta kama a Najeriya sun zama 111

by Dangalan Muhammad Aliyu
0 comments

Hukumar dake kula da cututtuka ta Najeriya, NCDC ta sake tabbatar da samun karuwar masu dauke da cutar Covid-19 guda 14 da daren yau Lahadi.

Kamar yadda hukumar ta bayyana a shafinta na yanar gizo gizo da shafin Twitter, tace adadin wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 111.

“A daren yau da misalin karfe 9:30, an sake samun masu dauke da cutar ‘Corona Virus’ guda14.”

Hukumar tace an sake samun 9 a jihar Legas, 5 a Abuja wanda ya hada jimillar wadanda aka tabbatar a Najeriya ya zama 111.”

Jerin adadin da aka tabbatar a kowacce jiha;

  • Lagos- 68
  • Abuja- 21
  • Ogun- 3
  • Inugu- 2
  • Ekiti- 1
  • Oyo- 7
  • Edo- 2
  • Bauchi- 2
  • Osun-2
  • Rivers-1
  • Binuwai- 1
  • Kaduna- 1


You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00