0
Rahotanni sun tabbatar da wani yaro mai shekara 5 kacal a duniya da ya kamu da cutar Kwabid-19 a jihar Niger.
Yaron da yake a karamar hukumar Chanchaga yana daga cikin mutum 13 da suka kamu rana daya a jihar.
Hakazalika matasa ‘yan rukunin shekaru 20 guda 3 suna cikin wadanda suka harbu da cutar a jiya Alhamis, ranar da cutar ta fi kama mutane a jihar.
Cikin wata sanarwa da kwamitin yaki da cutar a jihar Niger ya fitar, kwamitin ya bayyana cewa jumullar mutum 79 ne aka tabbatar da suna dauke da cutar Kwabid-19 a jihar.
Kwamitin yace an samu mutane 13 na ranar Alhamis a karamar hukumar Chanchaga baki daya, yayin da biyar daga cikinsu mata ne.
