Wakilan gwamnan Kano, Dr Abdullahi Ganduje da na dan takarar gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, sun hadu cikin farin da annashuwa yayin saukarsu a filin tashi da saukar jirage na Nnamdi Azikiwe dake birnin Abuja.
DABO FM ta tattara cewar a gobe Litinin, kotun kolin Najeriya zata yanke hukuncin karshe akan shari’ar zaben gwamnan jihar Kano da PDP da ‘dan takararta suke kalubalanta.

Gwamnan Kano, Ganduje, shine yayi nasara a kotunan korafin zabe da ta daukaka kara.
A wasu hotuna da suke yawo a shafukan sada zamunta, an dai hangi jagororin bangaren guda biyu yayin da suke sauka a birnin Abuja, suna cike da farinciki cikin girmama juna.
Haduwar da ta sha bambam da irin wacce ke hada masoyan wadannan jagorori duk da cewar sun fi kusa da kawunansu akan wandanda suke marawa baya. Haduwar magoya bayan da kusan mafiya yawan loktu take haddasa tashin hankula a tsakanin talakawan gari.
Hakan ne ma yasa aka dade ana kira ga al’umma da su kaunaci juna, sun bar illata junansu akan soyayya ko goyon bayan wani dan siyasa da kansu da su da ‘ya’yansu suke zama lafiya.
