1
Koton tarayya dake zamanta a Abuja, ta fatattaki karar da jam’iyyar PDP da kuma tsohon mataimakin shugaban kasar Najeriya Alh. Atiku Abubakar suka kayi gabanta. Karar dai suna kalubalantar nasara da shugaban Kasar Alh. Muhammad Buhari ya samu ne.Alkalai Bihar ne dai suka jagoranci zaman Kotun na Yau a babban birnin tarayyar kasar nan Abuja.
Alkalai biyar din da za su yanke hukunci a zaman kotun na yau sune:
·Mai Shari’a Abdul Aboki daga Abuja
·Mai Shari’a Joseph Ikyegh daga Benin
·Mai Shari’a Samuel Oseji daga Legas
·Mai Shari’a Peter Ige daga Abuja
·Mai Shari’a Muhammad Garba
