Home LabaraiGanduje ya mayar da Salihu Tanko Yakasai bakin aikinsa, kwana 18 bayan dakatar da shi

Ganduje ya mayar da Salihu Tanko Yakasai bakin aikinsa, kwana 18 bayan dakatar da shi

by Dabo Online
0 comments

Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da Salihu Tanko Yakasai, mataimakinsa na musamman kan harkokin yada labarai na zamani.

Tin dai a ranar 11 ga watan Okotba gwamna Ganduje ya dakatar da Salihu Tanko Yakasai sakamakon wasu kalamai da ya yi na ganin zagawar shugaba Muhammadu Buhari a kan damuwa da halin kunci da ‘yan Najeriya suke ciki.

Lamarin da ya janyo cece-kuce a shafukan sada zumunta musamman Twitter inda ‘yan Najeriya su ka yi wa gwamna Ganduje ca a kan dakatarwar.

 

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00