0
Gwamnan jihar Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje ya mayar da Salihu Tanko Yakasai, mataimakinsa na musamman kan harkokin yada labarai na zamani.
Tin dai a ranar 11 ga watan Okotba gwamna Ganduje ya dakatar da Salihu Tanko Yakasai sakamakon wasu kalamai da ya yi na ganin zagawar shugaba Muhammadu Buhari a kan damuwa da halin kunci da ‘yan Najeriya suke ciki.
Lamarin da ya janyo cece-kuce a shafukan sada zumunta musamman Twitter inda ‘yan Najeriya su ka yi wa gwamna Ganduje ca a kan dakatarwar.
