Tsohon gwamnan jihar Kano, Engr Dr Rabi’u Musa Kwankwaso yayi kira ga iyaye da su kulawa da ‘yayansu domin sauke nauyin da yake kansu.
Kwankwaso ya bayyana haka ne a sakon nuna murnar ga ranar da majalissar dinkin duniya ta ware wa yara duniya, “Ranar Yara” “Children’s Day”.
Sakon daya wallafa a shafinshi na twitter, Kwankwaso yace hakki ne daga wuyan iyaye dama al’umma wajen kula da tsare tarbiyya da Ilimin yara.
“Ya rataya a wuyan mu, mu hadu wajen kulawa, Ilimantar da ‘yayanmu domin su tashi cikin bin dokokinmu da al’adu a matsayinsu na manya masu daraja.
#ChildrensDay2019 Let us remember that our children are a trust on to us; it is our duty individually and collectively to nurture, educate and protect them, so that they grow up in obedience to our laws customs and traditions in excellence as productive adults. pic.twitter.com/odBlE0PyNw
— Rabiu Musa Kwankwaso (@KwankwasoRM) May 27, 2019