Shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya taya zababben Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje murnar nasarar da ya kara samu a kotin kare kukan ka.
Dabo FM ta tattara cewar sanarwar ta fito ta bakin mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu a yammacin Litinin bayan yanke hukuncin da kotin koli tayi na jaddada nasara ga gwamna Ganduje da Simon Lalung gwamnan Filato.
Buhari yace “Ina cikin farin cikin hukuncin da kotu tayi a cikin alfarmar jam’iyyar mu, APC dama can ita ta lashe zabukan kuma ta kara tabbatar wa a kotu, ba karamin faduwa bace idan muka rasa jihohi kamar Kano da Filato.”
Ya kara da cewa ” A wajen yan adawa idan suka samu nasara to adalci kenan, idan kuma ta juye musu anan magana zata sauya.”
Tini dai akayi ta murnar a jihar Kano, bangaren yan hamayya kuma ana ta zaman makoki.
