Home SiyasaDa Dumi Dumi: Rarara ya saki sabuwar waka tun gabanin hukuncin kotun koli

Da Dumi Dumi: Rarara ya saki sabuwar waka tun gabanin hukuncin kotun koli

by Muhammad Isma’il Makama
0 comments

Sanannen mawakin gambara na arewacin Najeriya, Dauda Kahuta Rarara ya saki sabuwar waka a jajiberin ranar yanke hukuncin kotun kare kukan ka.

Rahoton Dabo FM ya bayyana wakar ta fara yawo a kafafen sada zumanta ne a jajiberin yanke hukuncin zaben gwamnan jihar Kano wanda dan takarar jamiyyar PDP, Abba Kabir Yusif ya kara maka gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje a kotun Allah ya isa domin kalubalentar nasarar doron zaben da Ganduje yabi ya zama gwamnan jihar Kano.

Rararan ya fitar da faifan bidiyon wakar ne mai taken “Basa fahimta kuma basa da ganewa” wanda ke martani game da masu tinanin kotun zata iya kwacewa mai gidan sa a siyasa a yanzu kujerarsa.

You may also like

-
00:00
00:00
Update Required Flash plugin
-
00:00
00:00